Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Fajr ( The Dawn )
Choose the reader
Hausa
Sorah Al-Fajr ( The Dawn ) - Verses Number 30
هَلْ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍ ( 5 )

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?
الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلَادِ ( 8 )

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).
وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِ ( 9 )

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?
فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ ( 13 )

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.
فَأَمَّا الْإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلَاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِ ( 15 )

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."
وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلَاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِ ( 16 )

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."
وَلَا تَحَاضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ الْمِسْكِينِ ( 18 )

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!
وَجَاءَ رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا ( 22 )

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.
وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الْإِنسَانُ وَأَنَّىٰ لَهُ الذِّكْرَىٰ ( 23 )

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!
يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِي ( 24 )

Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌ ( 25 )

To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.
Random Books
- Kawar Da Shubha-
Formation : محمد بن عبد الوهاب
Source : http://www.islamhouse.com/p/339828
- TUSHE UKU NA MUSULUNCI-
Formation : محمد بن عبد الوهاب
Source : http://www.islamhouse.com/p/589
- RUKUNAN IMANI-
Formation : عمادة البحث العلمي بالجامعة الإسلامية
From issues : موقع الجامعة الإسلامية بالمدينة المنورة
Source : http://www.islamhouse.com/p/593
- SU WANE NE MASOYAN AHLUL BAITI ?SU WANE NE MASOYAN AHLUL BAITI ?
Source : http://www.islamhouse.com/p/156352
- SAKO ZUWA GA ALHAZAI DA 'YAN UMRA-
Source : http://www.islamhouse.com/p/156358