Hausa - Sorah An-Najm ( The Star )

Noble Quran » Hausa » Sorah An-Najm ( The Star )

Choose the reader


Hausa

Sorah An-Najm ( The Star ) - Verses Number 62
وَالنَّجْمِ إِذَا هَوَىٰ ( 1 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 1
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ ( 2 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 2
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
وَمَا يَنطِقُ عَنِ الْهَوَىٰ ( 3 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 3
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْيٌ يُوحَىٰ ( 4 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 4
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
عَلَّمَهُ شَدِيدُ الْقُوَىٰ ( 5 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 5
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.
ذُو مِرَّةٍ فَاسْتَوَىٰ ( 6 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 6
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
وَهُوَ بِالْأُفُقِ الْأَعْلَىٰ ( 7 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 7
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ ( 8 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 8
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ ( 9 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 9
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
فَأَوْحَىٰ إِلَىٰ عَبْدِهِ مَا أَوْحَىٰ ( 10 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 10
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
مَا كَذَبَ الْفُؤَادُ مَا رَأَىٰ ( 11 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 11
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
أَفَتُمَارُونَهُ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ ( 12 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 12
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
وَلَقَدْ رَآهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ ( 13 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 13
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.
عِندَ سِدْرَةِ الْمُنتَهَىٰ ( 14 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 14
A wurin da magaryar tuƙẽwa take.
عِندَهَا جَنَّةُ الْمَأْوَىٰ ( 15 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 15
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
إِذْ يَغْشَى السِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ ( 16 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 16
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
مَا زَاغَ الْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ ( 17 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 17
Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ آيَاتِ رَبِّهِ الْكُبْرَىٰ ( 18 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 18
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.
أَفَرَأَيْتُمُ اللَّاتَ وَالْعُزَّىٰ ( 19 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 19
Shin, kun ga Lãta da uzza?
وَمَنَاةَ الثَّالِثَةَ الْأُخْرَىٰ ( 20 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 20
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
أَلَكُمُ الذَّكَرُ وَلَهُ الْأُنثَىٰ ( 21 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 21
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
تِلْكَ إِذًا قِسْمَةٌ ضِيزَىٰ ( 22 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 22
Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.
إِنْ هِيَ إِلَّا أَسْمَاءٌ سَمَّيْتُمُوهَا أَنتُمْ وَآبَاؤُكُم مَّا أَنزَلَ اللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَانٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ وَمَا تَهْوَى الْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَاءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ الْهُدَىٰ ( 23 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 23
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
أَمْ لِلْإِنسَانِ مَا تَمَنَّىٰ ( 24 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 24
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
فَلِلَّهِ الْآخِرَةُ وَالْأُولَىٰ ( 25 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 25
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
وَكَم مِّن مَّلَكٍ فِي السَّمَاوَاتِ لَا تُغْنِي شَفَاعَتُهُمْ شَيْئًا إِلَّا مِن بَعْدِ أَن يَأْذَنَ اللَّهُ لِمَن يَشَاءُ وَيَرْضَىٰ ( 26 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 26
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
إِنَّ الَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ بِالْآخِرَةِ لَيُسَمُّونَ الْمَلَائِكَةَ تَسْمِيَةَ الْأُنثَىٰ ( 27 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 27
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
وَمَا لَهُم بِهِ مِنْ عِلْمٍ ۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا الظَّنَّ ۖ وَإِنَّ الظَّنَّ لَا يُغْنِي مِنَ الْحَقِّ شَيْئًا ( 28 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 28
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلَّا الْحَيَاةَ الدُّنْيَا ( 29 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 29
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
ذَٰلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ الْعِلْمِ ۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اهْتَدَىٰ ( 30 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 30
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
وَلِلَّهِ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الْأَرْضِ لِيَجْزِيَ الَّذِينَ أَسَاءُوا بِمَا عَمِلُوا وَيَجْزِيَ الَّذِينَ أَحْسَنُوا بِالْحُسْنَى ( 31 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 31
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
الَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَائِرَ الْإِثْمِ وَالْفَوَاحِشَ إِلَّا اللَّمَمَ ۚ إِنَّ رَبَّكَ وَاسِعُ الْمَغْفِرَةِ ۚ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ الْأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌ فِي بُطُونِ أُمَّهَاتِكُمْ ۖ فَلَا تُزَكُّوا أَنفُسَكُمْ ۖ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اتَّقَىٰ ( 32 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 32
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
أَفَرَأَيْتَ الَّذِي تَوَلَّىٰ ( 33 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 33
Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?
وَأَعْطَىٰ قَلِيلًا وَأَكْدَىٰ ( 34 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 34
Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?
أَعِندَهُ عِلْمُ الْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىٰ ( 35 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 35
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ ( 36 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 36
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
وَإِبْرَاهِيمَ الَّذِي وَفَّىٰ ( 37 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 37
Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?
أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٌ وِزْرَ أُخْرَىٰ ( 38 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 38
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
وَأَن لَّيْسَ لِلْإِنسَانِ إِلَّا مَا سَعَىٰ ( 39 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 39
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
وَأَنَّ سَعْيَهُ سَوْفَ يُرَىٰ ( 40 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 40
Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.
ثُمَّ يُجْزَاهُ الْجَزَاءَ الْأَوْفَىٰ ( 41 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 41
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ الْمُنتَهَىٰ ( 42 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 42
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
وَأَنَّهُ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىٰ ( 43 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 43
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
وَأَنَّهُ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَا ( 44 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 44
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
وَأَنَّهُ خَلَقَ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ ( 45 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 45
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ ( 46 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 46
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
وَأَنَّ عَلَيْهِ النَّشْأَةَ الْأُخْرَىٰ ( 47 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 47
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
وَأَنَّهُ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ ( 48 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 48
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
وَأَنَّهُ هُوَ رَبُّ الشِّعْرَىٰ ( 49 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 49
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.
وَأَنَّهُ أَهْلَكَ عَادًا الْأُولَىٰ ( 50 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 50
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
وَثَمُودَ فَمَا أَبْقَىٰ ( 51 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 51
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ ( 52 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 52
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
وَالْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىٰ ( 53 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 53
Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.
فَغَشَّاهَا مَا غَشَّىٰ ( 54 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 54
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ ( 55 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 55
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?
هَٰذَا نَذِيرٌ مِّنَ النُّذُرِ الْأُولَىٰ ( 56 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 56
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
أَزِفَتِ الْآزِفَةُ ( 57 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 57
Makusanciya fa, tã yi kusa.
لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ اللَّهِ كَاشِفَةٌ ( 58 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 58
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
أَفَمِنْ هَٰذَا الْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ ( 59 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 59
Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?
وَتَضْحَكُونَ وَلَا تَبْكُونَ ( 60 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 60
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
وَأَنتُمْ سَامِدُونَ ( 61 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 61
Alhãli kunã mãsu wãsã?
فَاسْجُدُوا لِلَّهِ وَاعْبُدُوا ۩ ( 62 ) An-Najm ( The Star ) - Ayaa 62
To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share