Hausa - Sorah At-Takwir ( The Overthrowing )

Noble Quran » Hausa » Sorah At-Takwir ( The Overthrowing )

Choose the reader


Hausa

Sorah At-Takwir ( The Overthrowing ) - Verses Number 29
إِذَا الشَّمْسُ كُوِّرَتْ ( 1 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 1
Idan rãna aka shafe haskenta
وَإِذَا النُّجُومُ انكَدَرَتْ ( 2 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 2
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
وَإِذَا الْجِبَالُ سُيِّرَتْ ( 3 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 3
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
وَإِذَا الْعِشَارُ عُطِّلَتْ ( 4 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 4
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
وَإِذَا الْوُحُوشُ حُشِرَتْ ( 5 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 5
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
وَإِذَا الْبِحَارُ سُجِّرَتْ ( 6 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 6
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
وَإِذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْ ( 7 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 7
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
وَإِذَا الْمَوْءُودَةُ سُئِلَتْ ( 8 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 8
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
بِأَيِّ ذَنبٍ قُتِلَتْ ( 9 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 9
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
وَإِذَا الصُّحُفُ نُشِرَتْ ( 10 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 10
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
وَإِذَا السَّمَاءُ كُشِطَتْ ( 11 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 11
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
وَإِذَا الْجَحِيمُ سُعِّرَتْ ( 12 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 12
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
وَإِذَا الْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ ( 13 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 13
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا أَحْضَرَتْ ( 14 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 14
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
فَلَا أُقْسِمُ بِالْخُنَّسِ ( 15 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 15
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
الْجَوَارِ الْكُنَّسِ ( 16 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 16
Mãsu gudu suna ɓũya.
وَاللَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ ( 17 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 17
Da dare idan ya bãyar da bãya.
وَالصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ ( 18 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 18
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ ( 19 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 19
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي الْعَرْشِ مَكِينٍ ( 20 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 20
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ ( 21 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 21
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ ( 22 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 22
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
وَلَقَدْ رَآهُ بِالْأُفُقِ الْمُبِينِ ( 23 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 23
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
وَمَا هُوَ عَلَى الْغَيْبِ بِضَنِينٍ ( 24 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 24
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَانٍ رَّجِيمٍ ( 25 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 25
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ ( 26 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 26
Shin, a inã zã ku tafi?
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ ( 27 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 27
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ ( 28 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 28
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
وَمَا تَشَاءُونَ إِلَّا أَن يَشَاءَ اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ ( 29 ) At-Takwir ( The Overthrowing ) - Ayaa 29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share