Hausa - Sorah Al-Layl ( The Night )

Noble Quran » Hausa » Sorah Al-Layl ( The Night )

Choose the reader


Hausa

Sorah Al-Layl ( The Night ) - Verses Number 21
وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ ( 1 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 1
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ ( 2 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 2
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ ( 3 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 3
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ ( 4 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 4
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَاتَّقَىٰ ( 5 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 5
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَىٰ ( 6 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 6
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَىٰ ( 7 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 7
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَىٰ ( 8 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 8
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَىٰ ( 9 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 9
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَىٰ ( 10 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 10
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّىٰ ( 11 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 11
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ ( 12 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 12
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالْأُولَىٰ ( 13 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 13
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ ( 14 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 14
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
لَا يَصْلَاهَا إِلَّا الْأَشْقَى ( 15 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 15
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ ( 16 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 16
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
وَسَيُجَنَّبُهَا الْأَتْقَى ( 17 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 17
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّىٰ ( 18 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 18
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰ ( 19 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 19
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
إِلَّا ابْتِغَاءَ وَجْهِ رَبِّهِ الْأَعْلَىٰ ( 20 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 20
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ ( 21 ) Al-Layl ( The Night ) - Ayaa 21
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).

Random Books

Choose language

Choose Sorah

Random Books

Choose tafseer

Participate

Bookmark and Share